Bangaren kasa da kasa; An gudanar da wani shiri na musamman kan wayar da kan mata musulmi dangane da hakkokin da mace ta ke da su a mahanga da dokoki na addinin Musulunci, wanda cibiyar kula da ayyukan mata ta kasar ta shirya gudanarwa.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, kamfanin dillancin labaran saba na kasar yeman ya habarta a shafinsa na yanar gizo cewa, an gudanar da wani shiri na musamman kan wayar da kan mata musulmi dangane da hakkokin da mace ta ke da su a mahanga da dokoki na addinin Musulunci, wanda cibiyar kula da ayyukan mata ta kasar ta shirya gudanarwa a garin Abin.
Bayanin ya kara da cewa dukkanin matan da suke halartar wannan shiri suna wakiltar kungiyoyi ne daban-daban na mata musulmi a lardunan kasar, wadanda za su isar da dukkanin abubuwan da suka koya yayin zaman ga sauran 'yan uwansa.
625835