Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Mostafa Safavi mataimakin shugaban kasa kan harkokin al'adu a wani taron manema labarai ya bayyana cewa, za a gudanar da tarukan makon nahjul balagha a kasashe hudu na duniya, wanda cibiyar kula da bunkasa harkokin al'adu da ilimi ta dauki nauyin shiryawa da kuma gudanarwa nan ba da jimawa ba.
A taron manema labaran da aka gudanar yau Mostafavi ya bayyana cewa hakika gudanar da irin wannan taro kan nahjul balagha yana da matukar muhimmanci a wannan lokaci.
Ya kara da cewa ilimin Imam Ali (AS) ilimi ne da dukkanin 'yan adam, wanda ya zama wajibi a watsa shi a duniya domin dora bil adama kan sahihin tunani na rayuwa.
630665