Kamfanin dillancin labarai na ikna da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran daga reshensa a yankin kudu maso gabacin Asiya ya watsa rahoton cewa; a daidai lokaci na fara azumin watan ramadana sallalin jama'a a n gudanar da sun e tare tsakanin musulmi yan shi'a da sunna a yankin Kashmir ba tare da shiga tsakanin jami'an tsaron Indiya ba a masallatan yankin. A ranar alhamis din da ta gabata ce dai ashirin da daya ga watan murdad musulmin yankin Kashmir suka fara gudanar da sallolin jama'a a tsakaninsu ba tare da nuna banbancin akida ko shiga tsakanin jami'an tsaron Indiya bad a hakan ke nuni matuka gayya da yadda aka samu ci gaba ta fuskar zaman takewa a wannan yankin.
632807