Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na idmedia an habarta cewa, an buga littafin nan mai suna Madina na babban sakataren kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a kasar Rasha, wanda aka buga a cikin harshen rashanci domin amfanin musulmin kasar.
Littafin dai ya kunshi bayanan da Auglo yake gabatarwa ne a dukkanin tarukan kungiyar OIC, da kuma jawabansa kan addinin muslunci a taruka daban-daban da aka gudanar a kasashen musulmi kimanin hamsin da bakwai.
642496