Bangaren kasa da kasa; an sanar da zama na ashirin da daya a baje kolin kur'ani na kasa da kasa da ake gudanarwa a birnin Tehran, tare da halartar wakilai daga cibiyoyin kur'ani da suke halartar baje kolin.
Kamfanin dillancin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, an sanar da zama na ashirin da daya a baje kolin kur'ani na kasa da kasa da ake gudanarwa a birnin Tehran, tare da halartar wakilai daga cibiyoyin kur'ani da suke halartar baje kolin na duniya.
Bayanin ya ci gaba da cewa, a yayain gudanar da zaman wasu daga malamai sun gabatar da jawabai kan mahangar kur'ani mai tsarki dangane da wasu batutuwa da dama da suke da dangantaka da matsayin kur'ani a rayuwar jama'a ta zamantakewa.
Jami'ar Al-Mostafa (SAW) ta duniya ita ce ta jagoranci shirya wannan zama tare da wakilanta da kuma sauran wakilan cibiyoyin addini.
646460