Bangaren kasa da kasa; Babban malamin addinin kirista na birnin Milan a kasar Italia ya bukaci da agina masallaci a cikin birnin, inda ya bayyana hakan da cewa hakkin musulmi ne su samu wuraren ibadarsu.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani bayani da ya nakalto daga jaridar zaman ta kasar Turkiya an habarta cewa, babban malamin addinin kirista na birnin Milan a kasar Italia ya bukaci da agina masallaci a cikin birnin, inda ya bayyana hakan da cewa hakkin musulmi ne su samu wuraren ibadarsu ba tare da tauye hakkokinsu ba.
Wannan kira ya z one a daidai lokacin da musulmin birnin suke kokawa a musamamn ma a lokutan Ramadan, sakamakon rashin masallatan da za su gudanar da sallar jama'a, wanda hakan ke ci musu tuwo a kwarya.
Musulmin sun kai kuka ga mahukunta inda aka bukaci jin tab akin manayan malaman addinin kirista na birnin, daga bisani kuma suka nuna amincewarsu.
649449