Bangaren kasa da kasa; Zamir Akram jakadan kasar Pakistan a majalisar dinkin duniya kuma jakadana kasar Pakistan a UN din ya yi kakkausar suka kwamitin kare hakkin dan adam na majalisar, kan rashin mayar da hankali kan kone kur'ani da wasu suka yi a Amurka.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin yanar gizo an bayyana cewa, Zamir Akram jakadan kasar Pakistan a majalisar dinkin duniya kuma jakadana kasar Pakistan a UN din ya yi kakkausar suka kwamitin kare hakkin dan adam na majalisar, kan rashin mayar da hankali kan kone kur'ani da wasu suka yi a Amurka a cikin 'yan kwanakin nan.
Zamir ya ce a lokacin da aka wulakanta addinin Musulunci ba cin zarafin wasu 'yan adam ban e, wadanda suke sama da biliyan daya da rabi a cikin duniya, domin kuwa kur'ani littafin da suke girmama wan e, amma da wani ya yi wani da ya saba wa siyasar turai, da tuni an an soke shi.
654502