IQNA

Taron Majalisun Dokokin Kasashen Musulmi A Ankara

14:10 - September 21, 2010
Lambar Labari: 1998639
Bangaren siyasa da zamantakewa; Majalisun dokokin kasashen musulmi za su gudanar da zamansu karakshin kungiyar hadin kan kasashen musulmi a birnin Ankara na kasar Turkiya.


Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar Al-ra'ay ta kasar Kuwait ta habarta cewa, majalisun dokokin kasashen musulmi za su gudanar da zamansu karakshin kungiyar hadin kan kasashen musulmi a birnin Ankara na kasar Turkiya da za a fara gudanarwa a cikin watan nan.

Taron zai samu halartar wasu daga cikin majalisun dokokin kasashen musulmi, inda za su mayar da hankali kan muhimman batutuwa da su ke ci musulmi tuwo a kwarya.

Yanzu haka dai wasu daga cikin 'yan majalisun dokokin kasashen musulmi sun fara isa birnin na Ankara domin halartar taron.

658978









captcha