IQNA

Jami'ar Al-Mostafa (SAW) Na Halartar Baje Kolin Sadarwa Na Digital

13:39 - October 10, 2010
Lambar Labari: 2009943
Bangaren kasa da kasa, Jami'ar Al-mostafa (SAW) na halartar baje kolin kasa da kasa na hanyoyin sadarwar ta hanayar digital da ake gudanarwa a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran.



Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na baje kolin kayyaykin dijital an bayyana cewa, Jami'ar Al-mostafa (SAW) na halartar baje kolin kasa da kasa na hanyoyin sadarwar ta hanayar digital da ake gudanarwa a birnin Tehran..

Bayanin ya ci gaba da cewa wannan baje koli na daya daga cikin irinsa mafi muhimmanci da ake gudanarwa a jamhuriyar Musulunci ta Iran a kowace shekara, inda kamfanoni daban-daban sukan baje kayayyakin sadarwa.

Yanzu haka dai jami'ar Al-mostafa (SAW) ta halarci wurin kuma ta baje wasu daga cikin kayyakin da za a iya yin amfani da su domin sadarwar Musulunci a kasashe daban-daban.

671057




captcha