Kamfanin dillancin labarai na Ikna da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar Musulunci ta Iran ya watsa rahoton cewa; a daidai wannan lokaci na Idin Ghadir Khum a ranar alhamis hudu ga watan Azar na wannan shekara ta dubu daya da dari uku da tamanin da tara hijira shamsiya a birnin Paris fadar mulkin kasar Faransa za a gudanar da shagulgulan sallatar wannan rana ta Idin Ghadir khum. Wadannan shagulgulan hadin guiwar kungiyoyin Beytolzahra suka shirya kuma wadannan kungiyoyi ne nay an shi'a da ke zaune a birnin Paris kuma za a samu halartar mambobin kungiyoyin da wakilan jamhuriyar Musulunci ta Iran day an yan jami'a faransawa da Iraniyawa da sauran ianiyawa mazuna kasar ta Faransa da duk wani mai sha'awa.
697764