Bangaren kasa da kasa, An sanar da lokacin fara gudanar da tarukan birnin Tilmisan bababr cibiyar musulunci da al'adunsa ta shekarar 2011, wanda za a gudanar a hukumance a kasar Aljeria tare da halartar manyan jami'an gwamnatin kasar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani bayani da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na El-watan an bayyana cewa, An sanar da lokacin fara gudanar da tarukan birnin Tilmisan bababr cibiyar musulunci da al'adunsa ta shekarar 2011, wanda za a gudanar a hukumance a kasar Aljeria tare da halartar manyan jami'an gwamnatin kasar ta Algeria.
Rahoton ya ci gaba da cewa Za a gudanar da zaman taron ne a matsayi na kasa da kasa, tare da halartar manyan jami'an gwamnatin kasar ta Algeria da suka hada da shi kansa shugaban kasar Abdulaziz Butaflika, tare da ministoci da kuma mataimakansa.
A bangare guda kuma na bayyana cewa taron zai samu halartar wakilai daga kasashen duniya daban-daban, da suka hada da na musulmi da kuma na larabawa, da kuma wakilan kungiyoyi na kasa da kasa.
720071