Bangaren kasa da kasa, a yau ne aka kammala zaman taron taron da aka gudanar a birnin Najaf mai alfarma na kasar Iraki mai taken Nahjul Balagha, wanda ya samu samu halartar masana daga sassa daban-daban na kasashen musulmi da na larabawa, inda aka gabatar da jawabai kan matsayin wannan littafi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Alkausar an bayyana cewa, a yau ne aka kammala zaman taron taron da aka gudanar a birnin Najaf mai alfarma na kasar Iraki mai taken Nahjul Balagha, wanda ya samu samu halartar masana daga sassa daban-daban na kasashen musulmi da na larabawa, inda aka gabatar da jawabai kan matsayin wannan littafi mai matukar matsayi a cikin al'ummar musulmi.
A wani bangaren kuma bayanin ya ci gaba da cewa wannan zaman taro ya samu karbuwa daga masana daga sassa daban-daban na kasar Iraki, kamar dubban masu ziyarar hubbaren Imam Hussain mai tsarki suka halarci wannan zaman taro a wasan kwaikwayo, wanda ke nuni da takamai abin da ya faru da zuriyar manzon Allah tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da iyalan gidansa.
An kammala wani taron wasan kwaikwayo da aka gudanar a birnin Karbala mai alfarma, wanda aka gudanar a kan waki'ar da ta faru da iyalan gidan manzon Allah (SAW) a karkashin jagorancin Imam Hussan (AS) wanda aka kammala a jiya a birnin mai alfarma.
766221