Kamfanin dillancin labarai na Ikna da ke kula da harkokin kur'ani a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa; yan sanda a kasar Faransa a ranar ashirin da hudu ga watan Urdebehesht shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya sun tarwatsa masu zanga'zangar nuna kin jinni da adawa da addinin musulunci a birnin Liyon .Wannan zanga-zanga dai kungiyoyin da ke nuna baker adawa da addinin musulunci suka shirya a birnin na Lion a wani mataki da nuni karara da yadda ake b=nuna banbanci da baker siyasa da adawa kan addinin musulunci a wannan kasa ta Faransa da ke yammacin turai.kuma wannan wani nmataki ne na nuna wariya da banbancin addini a fili.
791905