Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, a wani labari da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jam'iyar Alwifaq ta masu fafutuka a kasar Bahrain an bayyana cewa, an bude wani shafin internet domin tattara bayanai dangane da ayyukan ta'addanci na gidan sarautar kasar Bahrain a kan al'ummar kasar masu neman sauyi cikin harkokin siyasa da mulkin kasar, wadda take cikin yankin gabas ta tsakiya.
A wani labarin na daban kuma, jam'iyar Al-wifaq mai adawa a kasar Bahrain ta jaddada cewa babu gudu babu ja da baya wajen neman sauyi a cikin harkokin siyasa da mulki a kasar ta hanyar lumana, duk kuwa da matakan yin amfani da karfi kan 'yan adawa da mahukuntan kasar suke dauka.
A cikin wani bayani da jam'iyar ta Al-wfaq ta fitar jiya, ta bayyana cewa mahukuntan Bahrain da suke samun goyon bayan Amurka da Saudiyya, ba a shirye suke su saurari bukatun al'ummar kasar ba, a kan haka ne ma suke ta kara daukar sabbin matakai na muzguna wa masu neman sauyi a kasar,
Tare da taimakon sojojin Saudiyya da suke jibge a kasar domin murkushe fararen hula masu gudanar da zanga-zangar lumana. Bayanin ya ce jam'iyar ta Al-wifaq na nan kan bakanta na neman a baiwa al'ummar kasar damar gwamnatin da suke so.
A daren jiya ma dubban mutane sun gudanar da zanga-zangar lumana a garuruwa da daban-daban na kasar Bahrain, inda suka yi Allawadai da gwamnatocin Amurka da Saudiyya, wadanda suke da hannu kai tsaye wajen murkushe yunkurin neman sauyi a kasar.
843933