IQNA

Za A Gudanar Da Zaman Kan Abubuwan Suka Sanya Musulmi Mikewa

11:45 - August 18, 2011
Lambar Labari: 2173045
Bangaren kasa da kasa, ana shirin fara gudanar da wani zama kan mikewar musulmi a ckin kasashen larabawa domin 'yanci da sauyi a cikin harkokin siyasar wadannan kasashe, wanda zai gudana a wurin taron baje kolin kur'ani na kasa da kasa.


Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, rahoto daga masallacin Imam Khomeini (RA) ya yi nuni da cewa, yanzu haka ana shirin fara gudanar da wani zama kan mikewar musulmi a ckin kasashen larabawa domin 'yanci da sauyi a cikin harkokin siyasar wadannan kasashe, wanda zai gudana a wurin taron baje kolin kur'ani ginin da ke kan masallacin a babban birnin Tehran.

A yayin gudanar da wannan zama, wakilin babbar cibiyar ilimi ta birnin Qom Hojjatol-islam Dr. Zamani zai gabatar da jawabi ga mahalarta taron, danfane da wannan gagagrumin ci gaba da ake samu a halin yanzu a cikin kasashen larabawa da suke fama da shugabanni da sarakuna 'yan mulkin kama karya.

Tun bayan fara wannan bore a cikin kasashen larabawan dai, ya zuwa yanzu shugabanni biyu daga cikin masu mulkin Fir'annci sun bar mulki, da suka hada babban aminin Amurka da yahudawan sahyuniya a cikin kasashne larabawa.

845623


captcha