IQNA

Mutum Na Biyu A Gwamnatin Gaddafi Ya Hade Da 'Yan Tawayen Kasar

16:31 - August 21, 2011
Lambar Labari: 2174756
Bangaren kasa da kasa, mutum na biyu a cikin gwamnatin Gaddafi kuma tsohon fira ministansa ya balle ya shiga cikin gungun 'yan tawaye da suke dauke da makamai suna yakarsa tare da taimakon kungiyar tsaro.



Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya naklato wani rahoto daga jaridar Darul hayat cewa, mutum na biyu a cikin gwamnatin Gaddafi kuma tsohon fira ministansa ya balle ya shiga cikin gungun 'yan tawaye da suke dauke da makamai suna yakarsa tare da taimakon kungiyar tsaro a daidai lokacin da hare-harensu ke ta kara kusantar birnin Tripoli babban birnin kasar.

Tsohon fira ministan kasar Libiya Abdus-Salam Jalloud ya sanar da goyon bayansa ga masu bore a kasar ta Libiya.
Daya daga cikin na hannun daman Mu'ammar Gaddafi shugaban kasar Libiya dan kama karya Abdus-Salam Jalloud ya sanar da bijirewarsa ga gwamnatin Libiya karkashin jagorancin Gaddafi a jiya juma'a, tare da bayyana cikekken goyon bayansa ga Majalisar Wucin Gadi da ke wakiltan masu bore a kasar, kuma a halin yanzu haka ya mika kansa ga masu bore a garin Zintan bayan da ya tsere daga birnin Tripoli fadar mulkin kasar Libiya shi da iyalansa.
Abdus-Salam Jalloud ya rike mukamin fira ministan kasar Libiya a shekara ta 1972 zuwa 1977 kuma tsohon mamba ne a Majalisar juyin juya hali da Gaddafi ya jagoranta a shekara ta 1969 da ya kai shi ga mamaye madafun iko a kasar Libiya.
846577

captcha