Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto wani bayani daga shafin sadarwa na yanar gizo na NASIJ cewa, a cikin wani bayani da ya fitar babban malamin jami'ar Azhar a kasar masar ya mayar da martini kan wani malamin yahudawa da ya yi kira da a yi wa tsohon shygaban mulkin kama karya na kasar Masar Husni Mubarak afwa kan ayyukan day a tafka.
Ministan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ya sanar da cewa; haramtacciyar kasar Isra'ila ba zata amince kasar Masar ta jibge sojoji masu yawa a tsibirin Sina mallakin kasar ta Masar ba.
Jaridar shafinta na Internet ta bayyana cewar a jiya asabar ministan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila Ihud Barak ya sanar da cewar haramtacciyar kasar Isra'ila ba zata amince da shirin kasar Masar na jibge sojoji masu tarin yawa a tsibirin Sina da ke kusa da kan iyaka da Isra'ila ba.
A gefe guda kuma da ake bugawa a kasar Birtaniya a fitowarta ta ranar Juma'a ta bayyana cewa; Ihud Barak ya furta cewar idan gwamnatin Masar zata jibge sojojin masu yawa a tsibirin na Sina da nufin magance tashe tashen hankula da suke faruwa a kan iyakarta da haramtacciyar kasar Isra'ila ce, to babu matsala zata iya jibge sojojin domin hakan zai zame amfani ne ga Isra'ila.
854280