Kmafanin diallncin labaran iqna ya habarta cewa, a labarin da ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na IINA cewa, za a gudanar da zaman taro na wakilan majalisun dokoki na kasashen musulmi wadanda suke mambobi ne na kungiyar a garin Palambank na kasar Indonesia a cikin Fabrairun shekara mai zuwa ta dubu biyu da goam sha biyu, akmar dai yadda majiyar kwamitin hadin gwiwa na majalisun ya bayyana.
Kasar Iran bazata sake yarda da wani karin sassauci a mu'amalarta da hukumar a kan shirinta na makamashin nuklia ba, shugaban hukumar makamashin nukliayr kasar Iran Fridoon Abbasi ne, ya bayyanawa kamfanin dillancin labarun ISNA na kasar Iran a yau talata, kuma kara da cewa kasar Iran ta bada cikekken hadin kai ga hukumar kuma ta yi sassaunci kan lamura da dama wadanda basu zama tilas a kanta ba don tabbatarwa duniya gaskiyar shirin nata.
A ranar jumma'a da ta gabata ce shugaban hukumar ta ukiyo Amnao ya fitar da sabon rahoto kan shirin nukliyar kasar Iran, kuma an rarrabawa dukkan wakilan kasashen da suke hulda da hukumar guda 35 kofin rahoton. Kuma a ranar 12-satumba mai zuwa ne ake saran wadannan wakilai zasu tattauna kan rahoton.
860719