Bangaren kasa da kasa: Kotun daukaka kara a kasar Tunusiya a ranar ashirin da takwas ga watan Shahrivar na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya ta fitar da wani hukumci dangane da hukumta na kusa da kuma iyalan Zainul Abidina bin Ali tsohon shugaban kasar Tunusiya dan kama karya da kuma Ali Alsariyati mai kula da tsaron lafiyarsa kuma a ranar sha daya ga watan Mihir ne za a gurfanar da su.
Kamfanin dillancin labarai na ikna da ke kula da harkokin kur'ani mai girma a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa: : Kotun daukaka kara a kasar Tunusiya a ranar ashirin da takwas ga watan Shahrivar na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya ta fitar da wani hukumci dangane da hukumta na kusa da kuma iyalan Zainul Abidina bin Ali tsohon shugaban kasar Tunusiya dan kama karya da kuma Ali Alsariyati mai kula da tsaron lafiyarsa kuma a ranar sha daya ga watan Mihir ne za a gurfanar da su. Tun lokacin da masu zanga-zanga ta neman kawo sauyi da canji a kasar Masar suka hambarar da gwamnatin Zainul Abidina da kuma ya gudu ya bar ladansa a kasar ake kiran a gurfanar da shi da mukarrabansa da kuma iyalansa da leifukan kisa da kuma hamdamar dukiyar kasa.
864594