IQNA

Al'ummar kasar Bahrain Suna Yin Allawadai da Hukunci Kan Masu Bore

21:55 - October 01, 2011
Lambar Labari: 2196793
Bangaren kasa da kasa, dubban mutane ne suka gudanar da wata gagarumar zanga-zangar yin Allawadai da hukuncin da kotun soji ta yanke kan masu zanga-zanga a kasar Bahrain da suka hada da likitoci da jami'an kiwon lafiya, wanda hakan ya yi hannun riga da dokokin kasa da kasa.



Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar al-alam da ke gabatar da shirye-shiryenta a cikin harshen larabci kan tauraron dan adama daga birnin Tehran cewa, mutane ne suka gudanar da wata gagarumar zanga-zangar yin Allawadai da hukuncin da kotun soji ta yanke kan masu zanga-zanga a kasar Bahrain da suka hada da likitoci da jami'an kiwon lafiya, wanda hakan ya yi hannun riga da dokokin kasa da kasa da ma na duniya baki daya.

kotu a kasar Bahrain ta tabbatar da hukunci kan wasu mutane 14 da ake tsare da su saboda dalilai na siyasa, bisa hujjar cewa suna na hankoron kawo karshen mulkin mulukiya a kasar, dukkanin mutanen dai fitattu ne wajen gwagwarmaya ta siyasa a kasar ta Bahrain, da neman ma al'ummar kasar 'yancinsu daga mulkin mulukiya na gidan sarautar Ali-Khalifa.An yanke hukuncin daurin rai da rai a kan wasu daga cikinsu, wasu kuma daurin shekaru 15 a gidan kaso.

Kotun ta ce ta samu mutnanen da laifin tunzura mutane domin su yi zanga-zangar neman sauyi a kasar, da nufin kifar dagidan sarauta da kuma canja kundin tsarin mulki, da kuma hada baki da wasu bangarori na waje.

Wannan mataki da kotun ta dauka ya zo ne a daidai lokacin da mahukuntan kasar ta Bahrain suka kara tsananta matakan murkushe masu zanga-zangar lumana, da suke neman sauyi na demokradiyya a kasar, inda a cikin makon nan jami'an tsaron kasar Bahrain tare da na Saudiyya da suke taimaka musu, suka ci zarafin wasu mata saboda shiga cikin zanga-zangar neman sauyi, lamarin da ya jawo fushin al'ummar kasar da ma sauran musulmi a kasashen duniya daban-daban.

870051

captcha