IQNA

Gwamnatin Saudiyya Ta Kadu Matuka Sakamakon Farkawar Larabawa

19:39 - November 03, 2011
Lambar Labari: 2216963
Bangaren kasa da kasa, sabon yarima mai jiran gado a kasar Saudiyya ya fito karara ya bnuna kaduwarsu dangane da yadda musulmi da larabawa suke samun fadaka da ke kai su ga yin bore ga azzaluman shugabanninsu da sarakunansu.
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar rasid cewa, yarima mai jiran gado a kasar Saudiyya ya fito karara ya bnuna kaduwarsu dangane da yadda musulmi da larabawa suke samun fadaka da ke kai su ga yin bore ga azzaluman shugabanninsu da sarakunansu inda y abayyana cewa, ba za su taba amincewa mahajjata su yi amfani da damar aikin hajji wajen gudanar da wata zanga-zanga ba.
A bangare guda kuma babban limamin masallacin juma’a na garin ihsa Hashim Salman ya bayyana cewa, cin zarafin mabiya tafarkin iayalan gidan manzon Allah da wahabiyawan saudiyya ke yi babban abin kunya ga duniyar musulmi da ma rashin manufa ta rayuwa tare da bata surar musulunci a idon sauran al’ummomi na duniya kamar dai yadda muke ganin yanzu suna yi.
A cikin bayanan da suka gabata mun ji irin yadda munafukai suke yi wa manzon Allah zagon kasa domin kawo masa matsala a cikin lamarinsa na tafiyar da al’umma bisa koyarwar addinin muslunci, haka nan ma wannan aya mai albarka tana yin bayani ne kan yadda wasu munafukai suke yada jitajita tsakanin muminai da nufin raunana imaninsu, musamman ma kan batun yaki, da lamurin tsaro,
A lokaci guda kuma tana yi mana ishara da yadda ya zama wajibi a mayar da lamari ga wadanda su ne jagori na addini masu tsoron Allah da tsentseni da kuma sanin lamurra ta fuskar ilimi na addini, wadanda su ne za su iya warware matsaloli a cikin rayuwar zamantakewar musulmi.
891951


captcha