IQNA

Haramtacciyar Kasar Isra'ila Na Tattauna Batun Mayar Da Birnin Babban Birninta

19:23 - December 25, 2011
Lambar Labari: 2245015
Bangaren kasa da kasa, haramtacciyar kasar Isra'ila tana tattauna batun amincewa da wani daftarin doka da ke nufin amincewa da birnin Qods mai alfarma a matsayin fadar mulkin haramtacciyar kasar yahudawan sahyuniya.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habrta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na felesten cewa, Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ta sanar cewa a gobe majalisar Keneset za ta kada kuri'a kan wani daftarin doka da ke nufin amincewa da birin Qods a matsayin fadar mulkin gwamnatin yahudawan sahyuniya a hukumance.

Wannan daftarin doka dai yana mayar da birnin Qods fadar mulkin haramtacciyar kasar Isra'ila, tare da mayar da dukkanin harkokin siyasa da diplomasiyarta a birnin, da kuma mayar da palastinawa da suke cikin birnin saniyar ware. Tun a cikin watan Yulin shekara ta 1980 ne haramtacciyar kasar Isra'ila ta shelanta birnin Qods a matsayin babban birninta, amma amincewar majalisar Kenesent da daftarin doka zai mayar da birnin na Qods fadar mulkin gwamnatin yahudawan sahyuniya a hukumance.

A cikin wannan makon ne gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila ta amince da wani shiri na gina matsugunnan yahudawa 60,000 a cikin yankunan palastinawa da ke gabacin birnin Qods, lamarin da ya fuskanci kakkausar suka daga kasashen duniya daban-daban da suka hada har da na yammacin turai, amma Amurka taki amincewa da rashin halascin hakan, maimakon hakan ma ta hau kujerar naki a kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya a lokacin da dukkanin mambobin kwamitin suka amince da daftarin kudiri da ke yin Allawadai da HKIsra'ila kan mamayar yankunan palastinawa.

921504


captcha