Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na ONA News cewa, yanzu haka dai an shiga mataki na karshe a gasar karatu da hardar kur’ani mai tsarki da ake gudanarwa a birnin Maskat fadar mulkin kasar Oman daya daga cikin kasashen musulmi da ke yankin tekun fasha, da ke taka gagarumar rawa ta fuskar yada koyarwar kur’ani a tsaknain al’ummar kasar.
Wannan gasa dai tana samun halartar dalibai da makaranta gami da mahardata kimanin 285 daga sassa daban-daban na kasar, inda suke karawa da juna, kuma daga karshe za a fitar da sunayen wadanda suka lashe gasar a dukaknin bangarorin da aka gudanar da ita, inda za a bayar da kyautuka na musamman ga wadanda suka nuna kwazo.
Bayanin ya ci gaba da cewa an shiga mataki na karshe ne a gasar karatu da hardar kur’ani mai tsarki da ake gudanarwa a birnin Maskat fadar mulkin kasar ta Oman, bayan wuce sauran matakai da ake bi a lokacin gudanar da irin wannan gasa a sauran kasashe, inda yanzu ne za a gudanar da bita ta sauran bangarorin da suka rage a matsayin mataki na karshen gasar baki daya.
977144