Kamfanin dillancin labarai na ikna da ke kula da harkokin kur'ani mai girma a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa: a ranar bakwai ga watan Ordebehesht ne na shekara ta dubu daya da dari uku da tis'in hijira shamsiya abirnin Delhi No babban birnin kasar Indiya aka gudanar da wani taron binciken bukatar yanke alaka a tsakanin kasar da haramtacciyar kasar Isra'ila. A wajan wannan taron bincike dai an samu halartar malamai ,masana da jagororin addini da na siyasa da kuma na kungiyoyin kare hakkin dan adam n a na kasa da kuma suna bayyana dalailansu na bukatar kawo karshen dangantaka da ke tsakanin haramtacciyar kasar Isra'ila da kuma kasar ta Indiya kuma sun gabatar da dalilai masu karfi da suka shafi siyasa da zamantakewa da kuma kare hakkoki da mutuncin dan adama da kuma yin la'akari da hulda ta kasa da kasa.
994344