IQNA

Musulmin Rasha Sun Yi Allawadai Da Keta Alfarmar Manzon Allah (SAW)

17:36 - June 04, 2012
Lambar Labari: 2339909
Bangaren kasa da kasa, kungiyoyi da cibiyoyin musulmi na kasar Rasha sun yi kakakusar suka dangane da cin zarafin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan gidansa da makiya muslunci suke a sassa na duniya da sunan suna fadin albarkacin bakinsu ne ko bayyana ra’ayi.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na arabic.rt cewa kungiyoyi da cibiyoyin musulmi na kasar Rasha sun yi kakakusar suka dangane da cin zarafin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan gidansa da makiya muslunci suke a sassa na duniya da sunan suna fadin albarkacin bakinsu ne ko bayyana ra’ayi tare da bau kari daga gwamnatoci kan hakan.
Masu tsananin kiyayya da addinin muslunci a kasar suna ta kara tsananta kai hare-hare a kan masallatai da cibiyoyin addinin muslunci da ke kasar a mwani mataki na tsokana wanda suka rika dauka a lokutan baya inda har sukan kai hari kan kabrukan musulmi wqanda hakan ya samo asali daga mulkin da ya gabata.
A can kasar Azarbaijan kuwa wasu daga cikin musulmin kasar da suke da masaniya kan harkar yanar gizo sun shiga cikin wasu shafuka mallakin gwamnatin kasar da take tsananin gaba da addinin musulunci suka bata su a wani mataki na mayar da martani kan matakan takurawa ga mabiya addinin muslunci.
A wani labarin kuma an bayyana cewa wannan jam’iya tan ada manufofi na siyasa da suka yi daidai da mahnarta, ta yadda take son saka addini ya zama shi ne ma’anu a cikin dukaknin lamurranta na siyasa, haka nan kuma idan ta samu karbuwa a wajen al’ummar kasar tana sa ran za ta kawo gagarumin canji.

1021998

captcha