IQNA

Fadada Ilmomin Kur’ani Ga Sauran Alummomin duniya Shi Ne Aikin Malamai

13:53 - June 19, 2012
Lambar Labari: 2349843
Bangaren kasa da kasa, gudanar da muhimman ayyuka na fadada ilmomin kur’ani mai tsarki ga sauran al’ummomin duniya na daga cikin manyan ayyukan da suke agaban malaman addinin muslunci a koina cikin fadin duniya domin tabbatar da cewa sahihin sakon kur’ani ne ke isa ga sauran mutane na duniya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya naklato daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa, wasu daga cikin masana sun imanin cewa gudanar da muhimman ayyuka na fadada ilmomin kur’ani mai tsarki ga sauran al’ummomin duniya na daga cikin manyan ayyukan da suke agaban malaman addinin muslunci a koina cikin fadin duniya domin tabbatar da cewa sahihin sakon kur’ani ne ke isa ga sauran mutane na duniya musamman ma wadanda ba su da masaniya kan musulunci.
an bude wani ofishin kula da harkokin addini na kasar Kyrgystan a kasar Kuwait da nufin kara bunkasa harkokin addini da kuma kyakyawar alaka tsakanin kasashen ta fuskkar bunksa harkokin addini da ilim ga mi da al’adu a tsakaninsu kasantuwarsu mambobi a cikin kungiyar kasashen musulmi.
A cikin wanmnan makon ne wani mutum da ake kira mai bayar da fatawa na gwamnatin Saudiyya Abdulaziz Bin Abdullah Al-sheikh, ya fitar da wata fatawa daga mahangarsa ta akidar wahabiyanci da ke kafirta musulmi kansu wadanda ba su bin wannan tafarki na wahabiyanci, inda ya halasta kaddamar da kai hare-hare kan wuraren ibadar mabiya addinin kirista.
Masana da dama suka ganin a lokacin malaman addinin muslunci na hakika suke ci gaba da hankoron ganin an samu fahimtar juna tsakanin dukaknin al’ummomin duniya tare da zaman lafiya wasu daga cikin masu kiran kansu malaman addini a kasar Sudiyya suna fitar da fatawoyin halascin kai hari kan saura mutane da ba musulmi ba.
1032351
captcha