Kamfanin dillancin labarai na Ikna da ke kula da harkokin da suka shafi kur'ani mai girma a nan jamhuriyar musulunci ta Iran ne ya watsa rahoton cewa: Muhammad Albaltaji sakataren jam'iyar yanci da adalci da ke bangare ne na kungiyar siyasa na jama'atul Ikhwanul musulim a kasar masar ya bayyana cewa: gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila dole ta sani cewa lokacin fargaba da tsoron da kasar Masar ta ke yi mata ya kawar.An nakalto daga majiyar labarai ta Almanar cewa: sakataren jam'iyar yanci da adalci gwamnatin kasar Masar bat a neman tashin hankali da yanayi na dar dark o tashin hankali da wata kungiya ko gwamnati amma a daidai lokacin guda sabuwar gwamnatin kasar Masar ba kwanwar lasa b ace duk wanda ya hauta sai y arena kansa kuma za ta iya jurewa duk wani matsin lamba sai ta cimma abin da ta sanya a gaba. Ya kara da cewa; shiga da fita ba tare da neman iznin shiga a yankin hamadar Sina da mambobin gwamnatin Haramtacciyar kasar Isra'ila ke yi yana daya daga cikin abubuwan da za a sake yin dubi a cikinsa kuma ci gaba da barin wannan yanayi yana wanzuwa na barazana ga kasar Masar.
1043999