IQNA

Gwamnatin Kasar Kenya Ware wasu Kudade Domin Taimaka Ma Makarantun Kur’ani

14:32 - July 25, 2012
Lambar Labari: 2377445
Bangaren siyasa, gwamnatin kasar Kenya ta ware wasu kudade domin taimaka ma makarantun kur’ani da suke gudanar da harkoki na ilimin littafi mai tsarki tare da koyar da talibai karatunsa da kuma sanin kaidojin karatunsa kamar dai yadda sakataren ma’aikatar ilimi ta kasar ya sanar.

Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na bangaren yada labarai cewa, gwamnatin kasar Kenya ta ware wasu kudade domin taimaka ma makarantun kur’ani da suke gudanar da harkoki na ilimin littafi mai tsarki tare da koyar da talibai karatunsa da kuma sanin kaidojin karatunsa kamar dai yadda sakataren ma’aikatar ilimi ta kasar ya sanar da manema labarai.

A wani labarin na daban kuma mutanen kasar Ivory Coast yan gudun hijira wadanad aka kaiwa hari a sansaninsu da ke garin Dueku a daren jumma'a da ta gabata sun dorawa jami'an tsaron MDD wadanda suke gadin sansanin da laifin rashin karesu daga maharani, a daren jumma'an da ta gabat ce wasu mutanen dauke da kulake da kuma adduna su kimani 300 ne suka fadawa sansanin yan gudun hijirar wadanda suka kauracewa gidajensu sanadiyyar rikicin bayan zaben shugaban kasa na shekara ta 2010, suka kashe mutane 7 daga cikinsu sannan suka raunata wasu hamsin.

Wani dan gudun hijira wanda ya sami raunuka a harin na daren jumma'a mai suna Sidiki Kehi ya fadawa kamfanin dillancin labaran reuters cewa a lokacin da maharan suka zo, sun balle kofar shihga sansanin, suka fara keta tentunan da yan gudun hijira kimani suke cikinsa suna ta kona su, sidiki Kehi ya ce, ya guda ya je wajen jami'an tsaron wadanda suke gadin wurin, ya hau motarsu amma sai suke bankado shi ya fadi a kasa, inda maharani suka yi masa dukan kawo wuka, Allah ne kawai ya yi zai tsira da ransa inji shi.

Majalisar dinkin duniya ta samar da jami'an tsaro na UNOCI ne don kare wadan nan yan gudun hijira, amma sun kasa yin haka. Jami'an majalisar dinkin duniya dai sun ce ba zasu ce kome kan lamarin ba har sai sun kare bincike.

1061402





captcha