IQNA

Al’ummar bahrain Na Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-Zangar Neman Hakkokinsu

17:34 - August 01, 2012
Lambar Labari: 2383334
Bangaren kasa da kasa, al’ummar kasar Bahrain na ci gaba da gudanar da gangami a dukkanin yankunan kasar domin tabbatarwa mahukuntan cewa suna kan bakansu na neman hakkokinsu ba tare da wani sassauci ko saryar da hakkokinsu da aka haramta musu a matsayinsu an ‘yan kasa ba.
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Iba, cewa al’ummar kasar Bahrain na ci gaba da gudanar da gangami a dukkanin yankunan kasar domin tabbatarwa mahukuntan cewa suna kan bakansu na neman hakkokinsu ba tare da wani sassauci ko saryar da hakkokinsu da aka haramta musu a matsayinsu a ‘yan kasa ba wanda kuma abin da suke yi bai hannun riga da dokoki na kasa da kasa ba.
A wani labarin kuma dangane da kasar Sudan hukomomin kasar sun bayar da umurnin rufe dukkanin makarantu da ke birnin Nyala wanda shi ne babban birni a yankin Darfur ta Kudu inda a jiya aka gudanar da tarzoma tare da haddasa asarar rayukan mutane akalla 8. Wani gidan rediyo da ke garin na Nyala ya sanar a sanyin safiyar yau cewa gwamnati ce ta bayar da umurnin rufe makarantun domin hana ci gaba da zanga-zangar kin jinin gwamnatin Umar Hasan Albashir kamar dai yadda aka yi a jiya, kuma yanzu haka an barbaza dimbin jami'an tsaro a kan titunan birnin.
Tun dai a ranar 16 ga watan yunin da ya gabata ne aka soma gudanar da zanga-zangar kin jinin gwamnati a birane da dama na kasar ta Sudan, wannan kuwa bayan da gwamnati ta sanar da shirinta na tsuke bakin aljihu sakamakon matsalolin tattalin arziki da kasar ta fada.
1067173




captcha