Kmafanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Pakistan Today, cewa an bayyana kasar ta Pakistan a matsayin kasda take da babban dakin karatu wanda ya kunshi tsoffin littafai da suke da matukar tasiria cikin dukaknin harkoki na bincike da nazari kamar dai yadda aka tabbatar a cikin bayani da aka fitar bayan samu wasu dadaddun littafai da ak samu a wani dalkin karatu.
A wani lbarin kuma al’ummar birnin Mambai na kasar India sun gudanar da wata gagarumar zanga-zangar la’antar gwamatin Amurka da salon siyasarta kan al’ummomin uniya raunana da masu tasowa ta yadda suka bayyana Amurka da cewa ita bababr azzaluma da ke haddasa dukkanin matsaloli a duniya tare da saka kowa cikin matsaloli.
A yayin da ya ke gabatar da jawabinsa a lokacin ganawar, Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya bayyana yunkurin al'ummomin kasashen musulmi na kifar da shugabannin kama-karya ‘yan amshin shatan manyan kasashen duniya a matsayin lamari mai matukar muhimmanci sannan kuma wani mafari na yunkurin ganin bayan lalatattun cibiyoyin yahudawan sahyoniya da ma'abota girman kan duniya. Jagoran ya ci gaba da cewa: Sakamakon wannan yunkuri mai cike da albarka, da yardar Allah al'ummar musulmi za su sake dawo da daukaka, ‘yanci da kuma tsayin dakan da suke shi a baya.
Ayatullah Khamenei ya bayyana matasan kasashen musulmin a matsayin masu dauke da babbar bishara ga makomar al'ummar musulmi, daga nan sai ya ce: Farkawar da matasan kasashen musulmi suka yi, lamari ne da ke kara irin fatan da ake da shi na farkawar dukkanin al'ummar musulmi na duniya.
1096249