Shugaban na Iran ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke gabatar da jawabinsa a wajen taron kasa da kasa na malaman jami’oi da kuma farkawa ta Musulunci inda ya ce a daidai lokacin da ake tunani kan halin da Palastinawa suke ciki sakamakon irin mamayan da yahudawa suke musu, wajibi ne kuma a dinga tunani kan matsalolin da wasu mutanen suke ciki a kasashen Afirka, Amurka da sauran yankuna na duniya.
Shi ma a nasa bangaren babban sakataren taron farkawa ta Musulunci Dakta Ali Akbar Wilayati ya jinjinawa irin nasarar da al’ummar Gaza suka samu a kan yahudawa ‘yan share guri zauna cikin yakin kwanaki takwas da HKI ta kaddamar a Gaza inda ya ce hakan daya ne daga cikin sakamako na farkawa ta Musulunci da al’umma suka samu.
A yau ne dai aka bude wannan taron na kwanaki biyu wanda ya sami halartar masana da malaman jami’oi kimanin 350 daga ciki da wajen kasar Iran.
1150930