Sakamakon farko-farko da wasu kafafen watsa labarai da kuma wasu majiyoyi suka fitar suna nuni da cewa masu goyon bayan kundin tsarin mulkin su ne suke a kan gaba a yankuna daban-daban da aka gudanar da kuri’ar jin ra’ayin al’ummar. Wasu rahotannin ma suna cewa nasarar da masu goyon bayan kundin tsarin mulkin suka samu ya kai kashi 65%, duk da cewa za a sanar da asalin sakamakon kuri’ar ne a hukumance bayan an gudanar da zagaye na biyu na kuri’ar da za a gudanar a ranar asabar mai zuwa.
To sai dai kuma a daidai lokacin da ake ci gaba da kidayar kuri’ar, masu adawa da kundin tsarin mulkin sun zargi kungiyar Ikhwan al-Musulmin wadda shugaban kasar Masar din Muhammad Morsi ya fito daga cikinta da kokarin magudin zabe, a daidai lokacin da ‘yan Ikhwan din kuma suke zargin ‘yan adawar da amfani da kudi da kuma hanyoyi na karya wajen shafa kashin kaji ga kundin tsarin mulkin.
A jiya ne dai al’ummar Masar din suka fito don kada kuri’arsu kan sabon kundin tsarin mulkin kasar wanda ya janyo kace-nace da rikici a kasar. Rahotanni dai sun ce al’umma sun fito ainun lamarin da ya sanya aka kara sa’oin kada kuri’ar don ba da dama wa mutane kada kuri’arsu.
1154220