IQNA

Mayakan Kungiyar Boko Haram Na Ci Gaba Da Kai Hari Cikin Afirka

22:22 - August 16, 2015
Lambar Labari: 3344935
Bangaren kasa da kasa, mayakan kungiyar Boko Haram na ci gaba da kaddamar da harinta a cikin wasu yankuna na jahar Borno da ke arewacin Najeriya.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na TRT na kasar Turkiya cewa, wani dan kunar bakin wake da ake zaton dan kungiyar boko Haram ne ya kai hari a kasuwar wani kauye dake jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya.

Wannan lamari ya auku ne a  kauyen Rimirgo da ke karamar hukumar Askira Uba a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Nigeria inda rahoton ke  cewa  wani dan harin kunar bakin wake da ake kautata zaton dan kungiyar boko haram ne  ya tayar da jikidar bama- bamai da ke daure a jikinsa a wurin binciken ababen hawa na hadin gwiwa tsakanin 'yan Kato da gora da jami'an tsaro da ke farkon shiga kauyen.

Babu wani mutun da ya rasa ransa sanadiyar harin baya ga dan kunar bakin wake, saidai wani dan kato da gora tare da  wasu mutane biyu sun ji rauni.

Wannan Harin na zuwa ne a daidai lokacin da mai baiwa  shugaban Nigeria shawara kan harkokin tsaro Babagana Monguno ya jagoranci manyan hafsan Sojin kasar zuwa jihar Borno, a wani mataki na tabbatar da umarnin da shugaba Muhammadu buhari ya ba rundunar sojin kasar da su kawo karshen kungiyar  Boko Haram cikin watanni uku masu zuwa.

3344811

Abubuwan Da Ya Shafa: najeriya
captcha