Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin
sadarwa na yanar gizo na Alfurat News cewa, Amir Albayati kakakin ahlu
sunna na kasar Iraki ya bayyana cewa gwamnatin Saudiyya ta amince da
shiga Tsakani na Sheikh Mahdi Sumaidai babban mufti na Ahlu Sunnah a
Iraki kan hukuncin kisa a kan Sheikh Nimr wanda suka yanke masa.
Ya
ce gwamnatin ta Saudiyya ta tababtar musu da cewa ta amince da wannan
batu, kuma ministan harkokin wajen kasar ta Saudiyyah Adel Jubair ya
tuntubi sheikh Mahdi Sumaidai ta wayar tarho kan batun.
Amir Albayati
ya ce daga nan zuwa lokacin da ahlu Sunnah na kasar Iraki za su kammala
tattaunawa kan wannan batu, sarkin kasar saudiyya zai bayar da umarni
tattaunawa da su kan batun domin sanin abin da za a yi a tsakanin
bangarorin biyu.
A kwanakin baya ne dai kotn daukaka kara ta kasar
Saudiyya ta tabbatar da hukuncin kisa kan Sheikh Nimr, lamarin da yake
fuskantar kakkausar suka daga dukkanin bangarori na duniya.
Akn
wannan batu Muhammad Nimr dan uwan sheikh Nimr ya bayyana cewa, an mayar
da batun zuwa ga fadar sarkin masarautar al saud domin sa hannu kan
zartar da hukuncin kisa kan malamin, amma dai har yanzu ba su uffan kan
lamarin ba.
3470682