Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto
daga shafin Palastinu today cewa Wani daya daga cikin fitattun malaman
yahudawan Isra'ila ya yi kira ga sauran yahudawa mabiyansa da su fara
kona masallatai da majami'oin mabiya addinin kirista da suke cikin
birnin.
Shafin ya ce a wata zantawa da malamin yahudawan mai suna
Bent Scobchine ya yi da tashar talabijin mallakin gwamnatin yahudawan
Isra'ila ta Channel 2 ya bayyana cewa, dole ne su kawo karshen duk wata
alama ta wuraren bauta da ba na yahudawa ba a cikin birnin na Quds, da
hakan ya hada da masallatan musulmi da kuma majami'oin kirista.
Bayahuden ya ce addinin kirista addinin ne na bautar gumaka, saboda haka ba shi wurin zama a cikin wannan birni.
Wannan dai ba shi ne karon farko da wani malamin yahudawa ya yi irin wannan kira ga sauran yahudawan Isra'ila a kan musulmi da kiristoci dangane da kone wuraren ibadarsu ba.
Babban abin da
yafi dagawa musamman mabiya addinin kirsiata mazauan birnin Quds
hankali dai shi ne, yadda mutumin ya fito yana yin wannan kira kai tsaye
a gidan talabijin na gwamnatin Isra'ila ba tare da wata fagaba ba,
kamar yadda kuma babu wani mataki da aka dauka akansa a hukumance.
3471072