Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin
sadarwa na yanar gizo na Altafsir cewa, an gudanar da wannan zaman taro
ne bisa gayyatar jami’ar Aljinan da ke birnin, tare da halartar masana
da masu bincike daga jami’oi 20 na kasashen duniya.
A lokacin da yake
jawabi Zeglol Najjar malami a jami’ar ilmomon muslunci da ke kasar
Jordan ya bayyana cewa, tarjama kur’ani mai tsarkia cikin wasu yaruka
na duniya yana da babban tasiri wajen isar da ma’anar kur’ani.
Ya
kara da cewa gudanar da wanann bababn aiki tare da bayyana ma’anonin
kamlmomin kur’ani da kuma lafuzansa ga sauran al’ummomi na duniya ya
zama wajibi a wannan zamani, domin isar da sako ga al’ommomi da
harsunansu yana da tasirinsa mai yawa.
Daga karshen taron an fitar da
jawabin bayan taro da ke tabbatar da cewa masana da sauran malamai a
bangaren lamurra da suka danganci kur’ani daga koina aduniya dole ne su
mike domin isar da sakon kur’ani ga sauran al’ummomi ta hanyoyin da
suka dace, an kuma girmama Hashem Alayyubi shugaban jami’ar Jinan.
Kamar
yadda kuma bayanin bayan taron ya yi tsokaci kan wasu muhimman lamurran
da y ace ya zama wajibi su a mayar da hankali kansu, da hakan ya hada
gida cibiyoyin tarjama a kasashen duniya, da kuma samar da hanyoyi na
zamani wajen tarjama da watsa ta ga duniya, musamman ma hamyoyin zamani
na digital.
3471285