Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta
cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Alalam cewa,
Sheikh Jawad Alkhalisi ya bayyana cewa kawancen da Saudiyya ta kafa ban a
yaki da yan ta’addan Daesh ba ne, nayaki da hamas da Hizbullah ne da
kuma karfafa Isra’ila da sauran bangarori nay an ta’adda a yankin.
Wani
abin da ke kara sanya shakku cikin manufar Saudiyya kan kafa wannan
hadakar shi ne cewa a daidai lokacin da Saudiyyan take sanar da kafa
hadakar fada da ta'addancin, amma gwamnatocin kasashe wadanda suka
zamanto tungar 'yan ta'addan a halin yanzu suna zargin kasar Saudiyya.
Tana yin hakan tare da hadin gwiwan kasashe i wadanda su ma suna cikin hadakar, a matsayin kasashen da suke kan gaba wajen goyon bayan ayyukan ta'addancin da ke faruwa a yankin Gabas ta tsakiya musamman a kasashen.
A saboda haka ne da dama daga cikin masana da masu fashin bakin magana suke ganin manufar kafa wannan hadakar karkashin jagorancin Saudiyya ita ce kokarin rarraba kan al'ummar yankin bisa tushen kabilanci da mazhaba.
Haka nan kuma da
rufe irin danyen aikin da Saudiyya take yi na kirkirowa da kuma goyon
bayan kungiyoyin 'yan ta'adda a yankin Gabas ta tsakiya da ma sauran
yankuna na duniya wadanda a halin yanzu suka fara zama karfen kafa hatta
ga kasashen yammaci.
3471283