IQNA

Mutanen Bosnia Sun Tarbi Sabuwar Shekarar Miladiyyah Da Karatun Kur'ani

9:26 - January 03, 2016
Lambar Labari: 3480013
Bangaren kasa da kasa, mutanen kasar Bosnia sun tarbi sabuwar shekarar miladiyya ta 2016 da addu'oi da kuma karatun kur'ani mai tsarki, abiranan Sarayevo da kuma Kakani.
Kamfanin dilalncin labaran iqna ya nakalto daga shafin yada labarai na Arabi 21 ya bayar da rahoton cewa, mutanen kasar Bosnia wadanda akasarinsu musulmi ne, sun gudanar da tarukan adduoi da karatun kur'ani ne domin neman alkharan da ke cikin shekara da kuma neman tsari daga Allah kan dukkanin sharrukan da ke cikinta.
A yayin adduoin an gabatar da jawabai na jan hankali da kuma tunatarwa, inda bababn malami mai baar da fatawa na birnin Sarayevo Anas Liwakovic ya gabatar jawabi da a cikinsa yake cewa ya zama wajibi a kan musulmi su mayar da hankali ga addu'oi domin rokon Allah ya kawo bala'oin da suke fuskantar al'ummar musulmi a wannan duniya, na zalunci da kuma tarwatsa su da rarraba kawunansu da ake yi.
Daga karshe kuma ya yi jan hankali ga matasan musulmi da ake yaudararsu ana wanke kwakwalensu ta hanyar cusa musu muggan akidu na ta'addanci da sunan jihadi, inda sukan zama yan ta'adda tibran suna masu zaton cewa suna hidima ne ga addinin muslunci, alhali kuwa musulunci bai koyar da ta'addanci ga mabiyansa, bil hasali ma musulunci bai yi umarni da a tilasta wani ya yi addini ba.
3471382
captcha