Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin
sadarwa na Shamsu Arab cewa, Muhammad Nimr dam uwan Sheikh Nimr ya
bayyana cewa, haki sun girgiza bayan jin labarin cewa an zartar da
hukuncin kisa a kansa.
Ya ce ya san cewa dan uwansa mutum ne wanda
yake da karbuwa a wajen mutane da dama a duniya, kuma tabbas wannan aiki
na masarautar Saudiyya zai fuskanci mayar da martini, amma dai yana
bukatar hakan ya zama ta hanyar lumana.
A yau ne ma'aikatar harkokin
cikin gida ta kasar Saudiya ta sanar da cewa ta hanayar talabijin ta
kashe mutane 47 da suka hada da sheikh Nimr.
Mutane 45 daga cikinsu yan kasar Saudiyya ne daya kuma daga Masar, daya kuma daga kasar Chadi.
Wadannan
mutane 47 an kasha su a biranan Riyadh, Makka, Madina, Alsharqiyyah,
Alkasim, Hail, Asir, Aljauf, Najran, Baha da kuam Tabuk.
3472818