Bangaren kasa da kasa, cibiyar da ke bibiyar fatawowin takfiriyya da wadanda suka sha banban a Masar, ta gargadi Ikhwan da cewa su daina yin amfani da sunan jihadi a jerin gwanon tuna juyin 25 ga janairu.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto
daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar Almanar cewa, babbar cibiyar da ke
dakon fatawowin takfiriyya da wadanda
suka sha banban a kasar Masar ta gargadi yan kungiyar Ikhwan da cewa su daina
yin amfani da sunan jihadi domin kiran mutane zuwa jerin gwanon tuna juyin 25
ga janairu da za su yi.
Bayanin Darul fatwa na kasar Masar ya ce; yan kungiyar
ikhwan da wasu bangarori da suke da dangantaka da akidar takfiriyyahm suna ta
kiran magoya bayansu da su fito su yi jerin gwano domin tunawa da ranar juyin
juya halin kasar, domin yin hakan yana a matsayin jihadi, bayanin ya ce wannan
hankoro ne na tunzura jama’a domin tayar da hankali, wanda kuma ya sabawa doka.
Kungiyar Ikhwan dai an sakata a cikin kungiyoyin da aka
haramta akasar tare da sakata cikin ‘yan
ta’adda tun bayan kifar da Muhammad Morsi, kuma kungiyar ta mayar da ranar 25
ga watan Janairu a matsayin wata rana ta tunawa da juyin juya halin da aka yi a
kasar, tare da kiran jama’a da su fito domin tuawa da ita.
http://iqna.ir/fa/news/3467529