
Nan da wata daya da wani abu ne za a
gudanar da wannan taro, bayan da shugaban Palastinawa Mahmud Abbas ya bukaci
hakan, domin tattaunwa da kuma yin dubi kan halin da ake ciki a yankin.
Iyad Amin Madani bababn sakataren
kungiyar kasashen musulmin a cikin yan kwanakin da suka gabata ya yi dogwar
tattauwa tare da jami’an gwamnatocin Indonesia da kuma na Palastinu kan wannan
batu, domin sanin muhimman abubuwan da taron zai tattauna kansu.
Abubuwan da suke wakana a halin
yanzu na kisan palastinwa da keta alfarmar masallacin Quds na daga cikin
abubuwan da taron zai mayar da hankalia
kansu.
A cikin watan Disamban da ya gabata,
birnin Jakarta ya dauki nauyin wani taro mai alaka da batun Palastinu da kuma
halin da ake ciki.