IQNA

An Jaddada Wajabcin Yaki Da Tsatsaran Ra’ayi A Taron Morocco

22:32 - January 27, 2016
Lambar Labari: 3480082
Bangaren kasa da kasa, a taron da ake gudanarwa kan yaki da tsatsauran ra’ayi a tsakanin mabiya addinin muslunci a kasar Morocco an jaddada wajabcin shiga kafar wando da akidar ta’addanci.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa, ministocin kula da harkokin addini na kasashen musulmi a taron da suke gudanarwa kan yaki da tsatsauran ra’ayi a tsakanin mabiya addinin muslunci a kasar Morocco sun jaddada wajabcin shiga kafar wando da akidar nan ta tsatsauran ra’ayi da ke kai muslmi zuwa ga ta’addanci.

Ahmad Taufiq minister mai kula da harkokin addini a kasar Morocco ya bayyana a lokacin bude taron cewa, ya zama wajibi a kan dukaknin kasashen musulmi su dauki matakan da suka dace domin magance wannan matsala.

Shi ma a nasa bangaren Ahmd Juma’a tsohon mai bayar da fatawa na kasar Masar ya bayyana cewa, ya kamata majalisar dinkin duniya ta hada kai da kasashen domin fuskantar wannan lamari wanda yak e ciwa kowa tuwo a kwarya.

Shi ma Muhammad Yusuf ministan harkokin addini na kasar Pakistan ya jaddada cewa kasarsa ba za ta kasa a gwaiwa wajen ci gaba da fuskantar wannan lamari ba.

Baba Sisi ministan addini na Senegal ya irayi dukkanin kasashe da su bayar da hadin kai wajen ganin an yai tsatsauran ra’ayi, domin kacewa faruwar ayyukan ta’addanci da ke barazana ga kowa.

Abdullah Bin Bih shugaban kungiyar yada lamurran addaini a kasar UAE ya bayyana cewa, wannan aiki ya rataya  adukkanin kasashen duniya duniya, a kan haka a shirye suke s yi aiki da dukkanin kasashe domin tabbatar da wannan manufa.

Malamai 150 da kuma ministocin addini 40 daga kasashen duniya 100 ne suke halartar zaman taron, wanda yake samun halartar was bangarorin majalisar dinkin duniya da kuma kngiyoyi na kasa da kasa, wanda ake gdanarwa a kasar ta Morocco yanzu haka.

3470725

captcha