
Kamfanin
dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na
Sporting News cewa, Hussain Akbari jakadan Iran a kasar Libya cewa kimanin kashi
80 cikin dari na yan ta’addan Daesh da ke yakia
Libya yan kasashen waje ne da ska shigo ksar, amma kadan ne daga cikinsu
yan asalin kasar.
Akbari ya ci
gaba da cewa, da dama daga cikinmutanen Libya suna goyon bayan juyin juya halin
da aka yi a kasar, amma bas u goyon bayan abin da yake faruwa ahalin yanzu, inda yan ta’adda na kasashen
ketare suka mamaye komai a kasar.
‘yan ta’addan
Daesh suna da sabani da dukaknin bangarorin masu dauke da makamai a kasar Libya,
da hakan ya hada da wadanda suke rike da wasu yankuna ayammaci da gabashin kasar, wanda hakan ya
sanya suke da ta bata kashi a tsakaninsu.
Hussain
Akbari ya kara da cewa, kungiyar Alkaida tafi karfi a cikin kasar ta Libya,
saboda su yan kasar ne sun kan lagonta, amma Daesh suna shigo da mayaka daga
kasashen ketare ne.
Ya ci gaba
da cewa babban burin yan ta’addan daesh shi ne su mamaye wurare da suke da
arzikin danyen man fetur, kamar yadda yanzu haka wasu yankunan ke a karkashin
ikonsu, bayna da suka kori dakarun gwamnati.
Jakadan na
Iran ya ce babbar hanyar kawo karshen wannan rikici ita ce bayar da damar
zaunar da bangarorin da ke dake da makamai kan tebur da kuma sanya su ajiye
makamai.