IQNA

Kungiyar Alshabab Ta Dauki Alhakin Kaddamar Da hari A Gabshin Kenya

18:12 - January 28, 2016
Lambar Labari: 3480086
Bangaren kasa da kasa, kungiyar ‘yan ta’addan Alshabab da ta sanar da mika lamurra ga Daesh ta sanar da cewa it ace ke da alhakin kasashe jami’an tsaron gwamnatin Kenya.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na PressTV cewa, akalla mutane 5 ne daga cikin jami’an yan sandan kasar suka rasa rayukansu.

Joseph Bonet babban jami’in yan sanda na Kenya ya tabbatar da wannan bayani na kisan jami’an yan sandan kasar.

Tun kafin wannan lokacin dai kungiyar ta Alshabab ta sha alwashin kai munanan hare-hare a cikin kasar ta Kenya.

Wasu daga cikin wadanda suka shida abinda ya faru sun bayyana cewa an kai harin ne a lokacin da jami’an yansanda 10 ne a wurin.

Wannan harin yazo bayan wani makamancin sa da yan ta’addan na shabab suka kai yamma maso kudancin kasar a kwanakin baya, inda suka kashe mutane 8 daga cikin jami’an tsaro.

A cikin lokutannan dai mayakan na shabab sun tsananta harinsu kan jami’an tsaron Kenya, babu kakkautawa.

A cikin makonni biyu da suka gabata ma sun ce sun kashe sojojin Kenya  awani sansani na dakarun majalisar dinkin duniya a cikin kasar Somalia, amma har yanzu Kenya ba ta ce komai kan batun ba.

3470945

 

captcha