
Kamfanin
dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar
gizo na islamtoday.net cewa, gwamnatin kasar Mauritaniya ba tare
da wani Karin bayani ba, ta janye da batun rufe wasu daga cikin makarantun kur’ani
mai tsarki a lardunan Haud Sharqi da Haud Garbi.
Bayanin da
mahukuntan kasar suka bayar ya bayyana cewa makarantun da aka dakatar za su iya
ci gaba da gudanar da harkokinsu na karatu kamar yadda suka saba alokutan baya.
Tun kimanin
watanni biyu da suka gabata ne dai mahukunatn kasar Mauritaniya suka sanar da
cewa saboda yin amfani da ake da makarantun kur’ani wajen yada tsatsauran ra’ayi
sun rufe wasu makarantu.
Sheikh
Muhammad Alhassan Aldud shugaban babbar cibiyar harkokin addinin muslunci ta
kasar Mauritaniya ya bayyana cewa wannan mataki bai dace ba, kuma ya yi
kakakusar suka kan hakan, tare da kiran mahukuntan kasar da su canja shawara ba
tare da bata lokaci ba.
Y ace makarantun
kur’ani mai tsarki su ne izza da daukakakr kasar Mauritaniya, kuma rufe su
bababn kurta ne wanda baya da wani abin da zai wanke hukuma a kansa, a kan haka
suna bukatar a janye wannan mataki cikin gagagwa.