
Kamfanin
dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar
gizo na Alhurrah cewa, a jiya an bukaci da a kiyaye hakkokin mabiya addinai
marassa rinjaye a taron da aka gudanar a kasar Morocco kan kare mabiya addinai
marassa rinjaye a kasashen musulmi da suke rayuwa a cikinsu.
Wannan
taro ne an gudanar da shi a mataki na kasa da kasa, tare da halartar mutane
fiye da 300 da ska hada da malamai da masana da kuma ministocin kula da
harkokin addini na kasashen musulmi fiye da arbain, wanda suka tattauna kan
yadda za a kare hakkokin mabiya addinai mazauna kasashen muslmi.
Kafofin
yada labarai da dama a kasar ta Morocco sun bukaci mahalarta taron da sukafitar
da matasa guda daya, dangane da yadda ya kamata kasashen msulmi su dauki
matakan da suka dace wajen kare rayukan wadanda ba musulmi ba a kasashensu,
tare da wayar da kan masu tsatsauran ra’ayi kan cewa wannan ba maslaha ce ta addinin
muslunci ba.
A
nasu bangare mahalrta taron sun mika nasu sakonni ga gawmnatoci na kasashen
msuulmi domin daukar wannan mataki na kare mabiya addinai marassa rinjaye a
cikin kasashenu, kamar yadda kuma ska bukaci sauran kasashe wadanda musulmi ba
da su ma su kare rayukan musulmi a cikin kasashensu.