IQNA

Kwamitin Tsaron UN Da Azahar Sun Allawadai Da Harin Masallacin Imam Rida (AS)

21:34 - January 30, 2016
Lambar Labari: 3480092
Bangaren kasa da kasa, kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya gami da cibiyar addini ta Azahar sun yi Allawadai da kakkausar murya dangane da hari kan ‘yan shi’ar Najeriya.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na shin huwa cewa, a harin da aka kai kan masallacin Imam Rida (AS) a yankin Ihsa da ke gabacin Saudiyya mutane 4 sun rasu, wasu kimanin 18 sun jikkata.

A nasa bangaren kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya ya nuna damuwa kan abin da ya faru na kai wannan harin ta’addanci kamar dai yadda bayanin ya ce.

Kwamitin tsaron yay i kira ga kasashen duniya kan su taimaka ma gwamnatin Saudiyya wajen fuskantar wanann matasala.

Kamar yadda kuma ya bayyana hakan a matsayin aikin dabbanci da kisan gilla kan bil adama ba tare da rahma ba.

Cibiyar Azahar ita ma ta fitar da nata bayanin da ke cewa wannan ikin na barna, wanda ake kaiwa kan wuraren ibada, tare da keta alfarmarsu, wanda hakan ya yi hannun riga da koyarwar muslunci.

Wannan dai ba shi ne karo da aka kaddamar da harin ta’addanci kan mabiya mazhabar shi’a  ayankin ba.

3471367  

 

captcha