IQNA

Mutanen Bahrain Sun Gudanar Da Jerin Gwanon Tunawa Da Yunkurin Juyinsu

19:46 - February 18, 2016
Lambar Labari: 3480151
Bangaren kasa da kasa, dubban mutanen kasar Bahrain sun gudanar da gangami da jerin gwano domin tunawa da farmakin da jami’an tsaron kasar suka kai kansu a ranar wata alhamis shekaru biyar da suka gabata.

Kamfanin dillancin labaran Iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na tashar Alalm cewa, an gudanar da jerin gwanon ne a yankuna daban-daban na kasar, domin tunawa da ranar Alhamis ta fabrairun 2011, inda aka yi musu kisan kiyashi a dandalin Lu’alu’a a hannun jami’an tsaron kasar.

Masu gangamin sun yi ta rera taken cewa suna nan kan bakansu na neman sauyi a cikin harkokin siyasar kasar, inda suke bukatar suyi na dimukradiyya maimakon mulkin kama karya a kasar.

Mutane da dama ne suka yi shahada wasu kuma suka samu raunuka da suka hada da mata da kanan yara a kasar Bahrain, sakamakon matakan da mahukuntan kasar suke na ganin sun murkushe yunkurin al’ummar kasar, da ke neman a yi adalci a cikin lamarin mulki, da kuma neman hakkokinsu a matsayinsu na yan kasa.

3476655

captcha