IQNA

Sakon Gidan radiyon Kur’ani Na Kan Ta’aziyar Rasuwar Ustaz Ahmad Amir

16:54 - February 21, 2016
Lambar Labari: 3480159
Bangaren kasa da kasa, gidan radiyon kur’ani na kasar masar ya isar da sakon ta’aziyyar rasuwan bababn malamin kur’ani mai tsarki Ustaz Ahmad Muhammad Amir.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shfain sadarwa na yanar gizo na 3robanews.com Radiyo kur’an na kasar Masar ya bayar da rahoton rasuwar Ustaz Ahmad Muhamamd Amir, fitaccen makarancin kur’ani na kasar masar.

Sheikh Ahmad Muhammad Amir dai babban makarancin kur’ani mai tsarki a kasar Masar, ya rasu yana da shekaru 89 da haihuwa.

Wannan babban malami kuma makarancin kur’ani mai tsarki dan kasar Masar ya kasance daya daga cikin malaman da irinsa suka yi karanci a Masar ta fuskar karatun kur’ani da kuma iliminsa, inda ake kwatanta shi da malamai irin su Sheikh Muhammad Rif’at.

An Gudanar da Janazar Sheikh Ahmad Amir

Shafin sadarwa na yanar gizo na Veto a Masdar ya habarta cewa, Khalid Ahmad Amir dan mariyin ya bayyana cewa, an gudanar da janazarsa a masallacin Almajibi a garin Faqus da ke cikin lardin Sharkiyya, tare da halartar dubban malamai da kuma danginsa da almajiransa da sauran jama’ar gari.

Ya kuma kore wasu bayanai da ke cewa an rufe shi ne a garin Salihiyya wanda shi ne mahaifarsa.

3477216

captcha