Kamfanin dillancin labaran iqna ya
habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cibiyar yada al’adun
muslunc cewa, a jiya ne aka gudabnar da wani shirin talabijin a kasar Ghana kan
matsayin wilayat Faqih a jamhuriyar muslunci ta Iran wanda malam Idris Tupo ya
gabatar.
Bayanin ya ci gaba da cewa wannans hiri dai cibiyar kula da yada al’adun muslunci ta jamhuriyar muslunci ta Iran ce ta dauki nauyin gudanar da shi, inda tashar talabijin ta TV home bau ta dauki nauyin watsawa, inda aka yi bayani kan matsayin jagorancin malami wanda Marigayi Imam Khomeni (RA) ya kafa akasar Iran tun bayan samun nasar juyi.
Tare da bayyana matsayin Iran kan abubuwan da suke wakana a yankin gabas ta tsakiya da kuma tsayin Iran a kansu, musamamn ma a Bahrain, da Syria, da kuma kasar Yemen.
Haka nan kuma an yi baynai kan gudunmawar da jagora yake bayarwa wajen ganintsarin da Imam Khomei (RA) ya kafa ya ci gaba da tafiya, tare da bayyana cewa irin wanann tsari na shugabancin malami yana da babban tasiri a fagage da daman a zamantakewar al’umma musulmi, domin kuwa ana kare hakkokinta na musulunci da kuma yan adamtaka baki daya.